Wednesday, November 30, 2016

LABARUN DARE DUBU DA DAYA

Littafi ne da ya kunshi sabuwar fassarar dadadden littafin Larabawan nan mai suna ALFULAYLAH WA LAYLAH. An inganta fassararsa da daidaitacciyar Hausa, da kowane Bahaushe zai iya karantawa kuma ya fahimta.

Littafi ne da ya kunshi hikayoyi masu ratsa zukata, wadanda suka kunshi, tsantsar soyayya, jaruntaka da yaki, tsafe-tsafen mutanen dauri, duniyar aljanu da maridai, tatsuniyoyi, wa'azi da nasihohi, makirce-makircen maza da mata. Littafin ALFULAYLAH tumbin giwa ne, wanda babu irin labarun da babu a ciki.

Tuni mujalladi na farko ya shiga kasuwa. Maza hanzarta domin ku mallaki naku. Za a same shi a manya da kananan kantunan sayar da littattafai.


Haka kuma ga masu son karanta littafin dukkansa a Facebook (tun daga dare na 1 har zuwa dare na 1001), mun zube shi a cikin zauruka (groups) goma sha bakwai a Facebook, wanda za a iya biyan Naira dari biyu kacal (N200) domin shiga kowane zaure. Kada ku bari wannan dama ta wuce ku.

A tuntubi daya daga cikin masu fassarar, domin karin bayani game da yadda za a samu littafin, ko yadda za a biya kudin rijista:

Farfesa Malumfashi:
08035924022

Danladi Z. Haruna:
08030764060

Bukar Mada:
08021218337

6 comments:

  1. This comment has been removed by the author.

    ReplyDelete
  2. Na Dade ina kewan sanin karshen labarun dare dubu da daya sai yanzu Allah ya nufa zan samu.Allah ya saka muku da Alheri ya Kuma kara muku basira da nissan kwana Amin.

    ReplyDelete
  3. Na Dade ina kewan sanin karshen labarun dare dubu da daya sai yanzu Allah ya nufa zan samu.Allah ya saka muku da Alheri ya Kuma kara muku basira da nissan kwana Amin.

    ReplyDelete
  4. To wai, muda muke nesa daku sosai, yaya za'ayi mu sami littafin a hannu? Musamman mu da muke nan jahar kebbi!?

    ReplyDelete
  5. Wadanne shafuka ne zamu samu labarin?
    Ku bamu sunayensu

    ReplyDelete